Majalisa Za Ta Yi Zaman Gaggawa Saboda Zanga-zanga

Majalisar wakilan Najeriya za ta yi zaman gaggawa ranar Laraba, 31 ga Yuli, 2024 domin shawo kan masu zanga-zanga.

Hakan na kunshe ne a cikin wata takarda da manema labarai suka yi ido hudu da ita wadda magatakardan majalisar Dokta Yahaya Danzaria ya sanyawa hannu.

Dokta Yahaya Danzaria ya ce, “Bisa umarnin Kakakin majalisar, Honarabul. Abbas Tajudeen, PhD, ya ce a sanar da ku cewa za a yi zaman majalisa ranar Laraba 31 ga Yuli, 2024.

“Yana rokon ku, ku yi shirye-shiryen da suka dace don halartar taron, saboda za a tattauna muhimman batutuwa a wannan zama.

A farkon makon da ya gabata Ƴan Majalisar suka tafi hutu har zuwa ranar 17 ga Satumba, 2024.

Post masu alaƙa

Nafi’u ya gargaɗi Atiku ya daina sukar Tinubu da sunan ADC

Yan Sandan a Kano sun kama mutane 244, ciki har da 117 da ake zargi da fadan daba.

Ƴansanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a bikin Takutaha, tare da gargaɗin masu yunkurin tada zaune tsaye.