APC Ta Zargi Masu Zanga-zanga Da Niyyar Kifar Da Gwamnatin Tinubu

Alamar Jam'iyyar APC

Shugabannin jam’iyyar APC a jihohi 36 na Najeriya da kuma babban birnin tarayya Abuja, sun ce ba za su naɗe hannu suna gani a kifar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu da sunan zanga-zanga ba.

Da yake yi wa manema labarai jawabi a sakatariyar jam’iyyar APC ta kasa a ranar Litinin a Abuja, shugaban jamiyyar APC reshen jihar Kuros Riba kuma sakataren kungiyar Ciyamomin jam’iyyar a jihohi, Alphonsus Ogar Eba (esq), ya ce zanga-zangar ta kwanaki 10 da aka shirya, wani yunkuri ne na neman kifar da gwamnatin Tinubu.

Alphonsus Ogar Eba (esq) ya yi wannan jawabi ne a gaban shugabannin jamiyyar da suka fito daga jihohi 36 da Abuja, a wani yanayi da ke nuna goyon bayansu ga matsayar da ya bayyana.

A safiyar yau Litinin dai rahotanni sun tabbatar da cewa an kaddamar da zanga-zangar adawa da yunwa da tsadar rayuwa a jihar Neja.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya