Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci ta nuna takaici kan sauyi a dokar haraji

Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ta ce ta yi takaici dangane da zargin da ake ta yaɗawa cewa akwai banbanci tsakanin dokar haraji da ake son aiwatarwa a watan Janairun 2026 da wadda ƴan majalisar ƙasar suka amince.

A wata sanarwa da ta fitar, majalisar ta ce idan dai har hakan ya tabbata to babu abin da zai haifar illa janyo yanke ƙauna da raini daga al’ummar ƙasa.

Majalisar ta ƙara da cewa dalilin da ya sa al’amarin ya ba ta takaici shi ne sakamakon irin gudunmowar da ta bayar ga kundin na dokar harajin ƙasa.

Daga ƙarshe majalisar ta nemi ɓangarorin biyu na zartarwa da majalisar dokoki da su yi bincike domin gano yadda aka yi aka samu sauye-sauyen.

Post masu alaƙa

Kwankwaso ya amince a ba wa Kudu takarar Shugaban Kasa ta NDC

Yan sandan Kano sun shirya taron masu duwa da tsaki bayan zanga-zanga a Ungogo

Najeriya ta ƙarfafa ƙawancen tsaronta da Amurka