Ƙungiyar ƙwallon kafa ta Manchester City ta lashe kofin FA na shekarar 2026 bayan doke Chelsea 1-0.
Antoine Semenyo ne ya zura ƙwallon da ta bai wa Man City nasara bayan an dawo daga hutun rabin lokaci.
Wannan ne kofi na biyu da ƙungiyar ta lashe a kakar wasa ta bana bayan lashe kofin Carabao a baya-bayan na, inda take harin kofin Firimiya da Arsenal ke kan teburi.
Zuwa yanzu Pep Guardiola ya lashe kofuna 20 cikin shekaru 10 a Manchester City.