Man City ta lashe kofin FA bayan doke Chelsea 1-0

Ƙungiyar ƙwallon kafa ta Manchester City ta lashe kofin FA na shekarar 2026 bayan doke Chelsea 1-0.

Antoine Semenyo ne ya zura ƙwallon da ta bai wa Man City nasara bayan an dawo daga hutun rabin lokaci.

Wannan ne kofi na biyu da ƙungiyar ta lashe a kakar wasa ta bana bayan lashe kofin Carabao a baya-bayan na, inda take harin kofin Firimiya da Arsenal ke kan teburi.

Zuwa yanzu Pep Guardiola ya lashe kofuna 20 cikin shekaru 10 a Manchester City.

Post masu alaƙa

NDLEA reshen jihar Kano ta ƙone haramtattun ƙwayoyi kilo dubu 12.

Sojojin Najeriya sun ceto ɗalibai da malamai 10 da aka sace a Borno

An kama wasu mutum 7 da ake zargin ƙusoshin Boko-Haram ne a filin jirgin Katsina