Yusuf Buhari ya lashe zaɓen takarar majalisar tarayya a APC

Yusuf Buhari, ɗan tsohon shugaban Najeriya marigayi Muhammadu Buhari, ya samu nasara a zaben fitar da gwani na jam’iyyar APC na mazabar Sandamu/Daura/Mai’adua.

Da yake bayyana sakamakon zaɓen, shugaban kwamitin zaɓe na mazabar, Lawan Garba, ya ce Yusuf Buhari ya samu ƙuri’u 17,342, inda ya doke abokin takararsa, Auwalu Musa Daura, wanda ya samu ƙuri’u 480, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Saboda haka Garba ya ayyana Yusuf Buhari a matsayin ɗan takarar jmajalisar tarayya a am’iyyar APC na mazaɓar Daura/Sandamu/Mai’adua a zaɓe mai zuwa.

Sai dai a wata hira da manema labarai, abokin takarar Yusuf Buharin, Auwalu Lawan Daura, wanda ɗan tsohon shugaban hukumar DSS Lawal Daura ne, ya yi watsi da sakamakon zaɓen, inda ya yi zargin an tafka maguɗi.

A jawabin da Yusuf ya yi bayan nasarar, ya buƙaci magoya bayansa da abokin takarar su haɗa kai wajen samar da ci gaba a yankin.

Post masu alaƙa

Sanata ya bar APC a jajibirin zaɓen fidda gwani a Kebbi 

Dangote ya gana da Shugabar Tanzania kan batun gina sabuwar matatar mai a gabashin Afrika

An kama ɓarauniyar jariri a asibiti a Zamfara.