Wasu yan bindiga da ba a san ko suwaye ba, sun sace wani dan kasar chaina mai suna Yangi Ming, a birnin tarayya Abuja, inda suka nemi kudin fansar naira miliyan 300.
Rahotanni na cewa ,Yangi, yana aiki ne babban kantin Panda Supermarket, kuma an sace shi da misalin karfe 5pm sanye da gajeren wando mai launin ruwan kasa da bakar riga a yankin Durimi Abuja.
Wata yar uwarsa mai suna, A’isha Pan, mazauniyar Sharada Kano, ita ce ta samu kiran masu garkuwar da mutanen inda suka bukaci a biyasu naira miliyan 300 kafin su sake shi.
Kawo yanzu dai rundunar yan sandan birnin tarayya abuja , bata ce komai ba kan wannan lamari.
- Yadda Shagon Rahama Sa’idu Ya Kama Da Wuta
- Gwamnatin jihar Kano Ta Gargadi Yan Kasuwar Na’ibawa Yanlemo Kan Yin Bahaya A Wurin Siyar Da Mangoro.