Home » Masu Garkuwa Sun Nemi Kudin Fansa 300m Kafin Su Saki Dan Kasar Chaina Da Suka Sace A Abuja

Masu Garkuwa Sun Nemi Kudin Fansa 300m Kafin Su Saki Dan Kasar Chaina Da Suka Sace A Abuja

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Wasu yan bindiga da ba a san ko suwaye ba, sun sace wani dan kasar chaina mai suna Yangi Ming, a birnin tarayya Abuja, inda suka nemi kudin fansar naira miliyan 300.

Rahotanni na cewa ,Yangi, yana aiki ne babban kantin Panda Supermarket, kuma an sace shi da misalin karfe 5pm sanye da gajeren wando mai launin ruwan kasa da bakar riga a yankin Durimi Abuja.

Wata yar uwarsa mai suna, A’isha Pan, mazauniyar Sharada Kano, ita ce ta samu kiran masu garkuwar da mutanen inda suka bukaci a biyasu naira miliyan 300 kafin su sake shi.

Kawo yanzu dai rundunar yan sandan birnin tarayya abuja , bata ce komai ba kan wannan lamari.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?