Masu Zanga-Zanga Sun Fito A Biranen Najeriya

Masu zanga-zanga sun fito a biranen Najeriya domin kokawa kan halin da ƙasar ke ciki yayin da ƙasar ke bikin ranar dimkuraɗiyya a yau Alhamis.

A birnin Ibadan na jihar Osun masu zanga-zangar na ɗauke ne da allunan waɗanda suka ƙunshi saƙo daban-daban.

Daga cikin abin da masu zanga-zangar ke kokawa a kai akwai talauci da matsin rayuwa, waɗanda suke zargin manufofin gwamnati sun haifar.

Cire tallafin man fetur da sauye-sauye a ɓangaren kudi sun haifar da tashin farashin kayan masarufi da zubewar darajar kudin ƙasar, kamar yadda masana suka bayyana.

Sai dai gwamnatin ƙasar ta ce manufofin nata za su amfani a ƙasar a nan gaba.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya