Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya kawo ziyara jihar Kano

A yau ne Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya karɓi baƙuncin Mataimakin Shugaban Ƙasa Alhaji Kashim Shettima.

Kashim Shettima ya ziyarci Kano ne domin kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi dattijon jihar Alhaji Abubakar Imam Galadanchi.

A cewar wata sanarwa dauke da sa hannun sakataran yada labaran Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ta ce, Mataimakin Shugaban kasar zai samu tarba daga Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf.

Tun da sanyin Safiya dai ake ta dakon isowar Mataimakin Shugaban Ƙasar, amma har kawo lokacin haɗa wannan rahoto bai iso filin jirgin Malam Aminu Kano da ke nan Kano ba.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr