• Home  
  • Matasa Sun Kaddamar Da Zanga-Zanga A Jihar Neja
- Babban Labari - Labarai

Matasa Sun Kaddamar Da Zanga-Zanga A Jihar Neja

Masu zanga-zangar sun fantsama kan manyan titunan jihar, ciki har da babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna.

Masu zanga-zanga a Neja

Matasa a Jihar Neja sun kaddamar da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya.

Masu zanga-zangar sun fantsama kan manyan titunan jihar, ciki har da babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna.

Matasan da ke tafe suna rera wakar adawa da tsare-tsaren gwamnati sun daga kwalaye masu dauke da rubutu a jikinsu da ke nuna bacin ransu kan halin tsadar rayuwa a Najeriya.

A jikin kwalayen sun yi rubuce-rubuce da dama, da suka hada da, ‘A soke tsare-tsere masu kuntata wa jama’a; ‘tura ta kai bango’; ’ ‘Mu Ba Bayi Ba Ne A kasarmu’; ‘Ba Za Mu Jere Wannan Wahalhalun Ba’, ‘Dole A Dawo da tallafin man fetur’.

Gwamnatin tarayya da na jihohi sun yi yunkuri iri-iri da zummar dakatar da zanga-zangar, suna masu cewa zauna-gari-banza da makiya dimokuradiyya za su iya kwace ta, wadda ka iya janyo asara ga kasar.

A baya dai rahotanni sun tabbatar da cewa za a fara zanga-zangar ne ranar Alhamis, 1 ga watan Agustan, 2024.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000