• Home  
  • APC Ta Zargi Masu Zanga-zanga Da Niyyar Kifar Da Gwamnatin Tinubu
- Babban Labari - Labarai

APC Ta Zargi Masu Zanga-zanga Da Niyyar Kifar Da Gwamnatin Tinubu

Shugabannin jam’iyyar APC a jihohi 36 na Najeriya da kuma babban birnin tarayya Abuja, sun ce ba za su naɗe hannu suna gani a kifar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu da sunan zanga-zanga ba. Da yake yi wa manema labarai jawabi a sakatariyar jam’iyyar APC ta kasa a ranar Litinin a Abuja, shugaban jamiyyar […]

Alamar Jam'iyyar APC

Shugabannin jam’iyyar APC a jihohi 36 na Najeriya da kuma babban birnin tarayya Abuja, sun ce ba za su naɗe hannu suna gani a kifar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu da sunan zanga-zanga ba.

Da yake yi wa manema labarai jawabi a sakatariyar jam’iyyar APC ta kasa a ranar Litinin a Abuja, shugaban jamiyyar APC reshen jihar Kuros Riba kuma sakataren kungiyar Ciyamomin jam’iyyar a jihohi, Alphonsus Ogar Eba (esq), ya ce zanga-zangar ta kwanaki 10 da aka shirya, wani yunkuri ne na neman kifar da gwamnatin Tinubu.

Alphonsus Ogar Eba (esq) ya yi wannan jawabi ne a gaban shugabannin jamiyyar da suka fito daga jihohi 36 da Abuja, a wani yanayi da ke nuna goyon bayansu ga matsayar da ya bayyana.

A safiyar yau Litinin dai rahotanni sun tabbatar da cewa an kaddamar da zanga-zangar adawa da yunwa da tsadar rayuwa a jihar Neja.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai