Mutanen Da AmbaAliyar Ruwa Ta Kashe A Neja Sun Kai 110

Alkaluman waɗanda ambaliyar ruwa ta kashe a jihar Neja ya kai mutum 110, a cewar hukumar ba da agajin gaggawa na jihar.

Masu aikin ceto sun ce sun gano gawawwaki da dama.

Jami’ai a yankin Mokwa wurin da lamarin ya faru, sun yi gargaɗin cewa ƙarin mutane na cikin barazana a birnin.

An shafe tsawon sa’o’i ana tafka mamakon ruwan sama a yankin ranar Laraba, inda ruwa ya tafi da gidaje aƙalla 50.

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin yiwuwar samun ambaliya a kusan rabin jihohin ƙasar 36.

Sama da mutum 1,200 ne suka mutu sakamakon ambaliya a bara sannan sama da miliyan ɗaya suka ɗaiɗaita, a ambaliyar da ba a taɓa gani ba cikin gomman shekaru.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya