Mutanen da suka mutu a haɗarin kwale-kwale a Sokoto sun kai 48

Kimanin mutum 48 ne suka mutu yayin da ake ci gaba da neman yara 12 bayan haɗarin jirgin ruwa da ya faru a yankin Goronya da ke jihar Sokoto.

Akasarin waɗanda lamarin ya rutsa da su yara ne waɗanda ke kan hanyar zuwa gona a safiyar jiya Alhamis.

A tattaunawarsa da BBC, ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Gada da Goronyo a majalisar wakilan Najeriya Bashir Gorau ya ce a halin yanzu masu ninkaya na ci gaba da aikin ceto domin ganin ko za a samo sauran yaran da suka ɓace da ransu.

“Akasarin waɗanda abin ya rutsa da su yara ne da mata, yara ƴan ƙasa da shekara 10,” a cewar Gorau.

“Rafi ya raba mutanen ƙauyen da gonakinsu, shi ya sa a kodayaushe mutane ke amfani da kwale-kwalen katako domin zuwa gona,” kamar yadda ɗan majalisar ya yi ƙarin haske.

A Najeriya ana yawan fuskantar hatsarin kwale-kwale wanda ke laƙume rayuka musamman a yankunan karkara.

Lamarin ya fi ƙamari ne a lokacin damina, inda rafuka kan cika da ruwa, sannan kuma babu wasu matakan kariya da ake amfani da su wajen irin wannan sufuri, haɗi da rashin ingancin kwale-kwalen.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta fara gina sabuwar fadar Sarkin Dutse kan N2.6bn

NOA da JCI Abuja Unity sun ƙaddamar da shirin wayar da kan jama’a kan tsaron hanya

Gwamnatin Jigawa za ta haɗa gwiwa da Masar kan noman dabino da dankali