Na fi shugaba Tinubu saka kaya masu tsada, tun da na hadu da shi agogonsa daya yake amfani da shi.” – Kashim Shettima.

Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya bayyana cewa shugaba Tinubu mutun ne mai tawali’u da ƙanƙan da kai kuma bai yarda da al’mubazzaranci ba.
A cewar wata majiya, Shettima ya bayyana hakan ne ranar Alhamis a wani taron ƙaddamar da littafi a Abuja. Ya ƙara da cewa gidansa na Maiduguri ya fi gidan Tinubu na Legas.
“Tinubu shugaba ne da za mu iya bai wa yardarmu , ba maganar siyasa nake yi ba, yana nufin mutanen Najeriya da alheri, ba kuma ya zo mulki ba ne don ya tara abin duniya.” a cewar Shettima.

Post masu alaƙa

Kotu ta dage hukunci kan shari’ar datse yatsa bisa alkawarin naira miliyan 80.

Ba za mu dawo da tallafin man fetur ba —Fadar Shugaban Ƙasa

An Kashe Makiyaya 50 An Sace Shanu Sama da Dubu 2 A Kaduna — MACBAN