Najeriya ta doke Iran da ci 2 a wasan sada zumunta

Tawagar ƙwallon ƙafa ta Najeriya, Super Eagles, ta doke ƙasar Iran da ci 2 da 1 da wasan sada zumunta da suka buga a ranar Juma’a.

Ƙasashen biyu sun kara da juna a filin wasa na Mardan Sport Complex da ke yankin Antalya na ƙasar Turkiyya.

Ɗan wasan gaban Super Eagles, Moses Simon ne ya fara jefa ƙwallo a raga a minti 6 da fara wasan.

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Akor Adams ya jefa wa Najeriya ƙwallo ta biyu a raga a minti ma 51.

Shi kuma ɗan wasan gaban ƙasar Iran Mehdi Taremi ya jefa wa ƙasarsa ƙwallo a raga.

’Yan wasan Super Eagles, Samuel Chekwueze da Ademola Lookman ne suka taimaka wajen jefa wa Super Eagles ƙwallaye biyu a raga.

Fitaccen ɗan wasan gaban Super Eagles, Victor Osimhen bai samu buga wasan ba sakamakon raunin da ya samu a hannunsa a wasan da Galatasaray ta yi da Liverpool a Gasar Zakarun Turai.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya