Netumbo Nandi Ta Zama Mace Ta Farko Da Zata Jagoranci Shugancin Kasar Namibia

An rantsar da Netumbo Nandi-Ndaitwah a matsayin shugabar ƙasar Namibia, wadda ta kafa tarihin zama mace ta farko da za ta jagoranci ƙasar.

Tshohuwar ministar harkokin wajen ƙasar ta kasance jajirtaciyyar ƴar jam’iyyar SWAPO wadda ke mulkin Namibia tun bayan samun ƴancin kai daga Afirka ta Kudu a 1990.

Da take magana da BBC, Nandi-Ndaitwah ta yarda da cewa wasu za su iya sukarta saboda jinsinta maimakon ayyukan da take yi – sai dai ta ce za ta ci gaba da yaƙi da cin zarafin jinsi.

Netumbo ta shiga cikin jerin matan Afirka ƙalilan da suka jagoranci ƙasarsu tun lokacin da Liberia ta zaɓi shugabar ƙasa ta mace ta farko shekaru 20 da suka wuce.

Post masu alaƙa

Kotun ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar ADC

Babu wata kotu da ta wanke Murtala Sule Garko daga zargin badaƙalar kudi – Baba Jibo

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta raba Naira miliyan ɗaya ga matasa 36 a shirin haɗin gwiwa na magance aikata laifuka