• Home  
  • NNPC na shirin ba wa wasu kamfanoni damar shiga harkokin samar da man fetur a Najeriya
- Labarai

NNPC na shirin ba wa wasu kamfanoni damar shiga harkokin samar da man fetur a Najeriya

Shugaba kamfanin na NNPC Mele Kyari ya ce, nan ba da dadewa ba farashin zai sauko idan aka sami wasu kamfanoni da za su shiga a dama da su wajen samar da man.

NNPC na shirin ba wa wasu kamfanoni damar shiga harkokin samar da man fetur a Najeriya

Kamfanin man fetur na kasa NNPC ya ce, nan ba da jimawa ba, zai janye daga mallakar da ya yi a kan kayayakin man kasar nan.

Wannan na zuwa ne kwana guda bayan da kamfanin ya rubanya farashin litar man fetur a gidajen mai mallakar kamfanin.

Shugaba kamfanin na NNPC Mele Kyari ya ce, nan ba da dadewa ba farashin zai sauko idan aka sami wasu kamfanoni da za su shiga a dama da su wajen samar da man.

Wannan dai na zuwa ne bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cewa, gwamnati ta dakatar da tallafin man fetur.

Tun bayan wannan furuci na sabon shugaban ne aka fara samun dogayen layi a gidajen sayar da mai.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai