NOA Ta Bukaci Masana’antar Fina-finai Ta Inganta Dabi’u Da Martaba Nijeriya.

Hukumar wayar da kan jama’a ta kasa, NOA, ta bukaci kungiyar masu shirya fina-finai data yi amfani da masana’antar wajen inganta dabi’u da al’adu da martaba Nijeriya.

Darktan Janar na hukumar, Mallam Lanre Issa-onilu, ne ya bayyana hakan lokacin da ya karbi mambobin kungiyar reshen babban birnin tarayya Abuja.

Mallam Lanre, ya ce fina-finai suna da tasiri sosai wajen chanja tunani da kuma hada kan kasa , inda ya shaidawa tawagar cewa hukumar NOA na shirin hada kai da masana’antar fina-finan don wayar da kan jama’a cikin shirye-shiryensu na film.

Shugaban masu shirya fina-finai reshen babban birnin tarayya Abuja, Desmond Utomwen, ya yabawa hukumar kan kokarin da take yin a wayar da kan jama’a da inganta dabi’u tare da yin alkawarin hada kai da hukumar don fito da fina-finai da za su wayar da kan yan kasa da suka shafi inganta dabi’u da kishin kasa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *