Home » Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Ci Mutane Biyu A Jigawa

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Ci Mutane Biyu A Jigawa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwmnan Jihar Jigawa, Umar Namadi Dan Modi

Rundunar ƴan sandan Najeriya a jihar Jigawa ta ce an samu  mummunan rikici tsakanin manoma da makiyaya a ƙaramar hukumar Birnin Kudu.

An ce lamarin ya yi sanadin mutuwar mutum biyu da ƙona wasu gidaje uku.

‘Yan sandan sun ce sun kama mutum biyar da hannu a afkuwar rikicin, inda ake ci gaba da gudanar da bincike a kansu.

Shaidun gani da ido sun bayyanawa manema labaru cewa makiyayan sun gayyato takwarorinsu daga jihar Katsina inda suka shiga yankin da shanunsu suka kuma lalata gonaki da dama. 

kakakin rundunar ƴan sanda a jihar Jigawa, DSP Lawan Shiisu Adam, ya ce jami’ansu da hadin gwiwa da jami’an hukumar tsaro ta civil defense da kuma ƴan vigilante sun kai ɗauki yankin,  tare da tarwatsa masu rikicin.

Ya ce sun gano shanu 15 da aka gudu aka bari a wurin.

A cewarsa, rundunar ta aike jami’anta tare da ƴan vigilante domin tabbatar da zaman lafiya da hana ruruwar rikicin.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?