• Home  
  • Ruwa Ya Yi Gyara A Bunkure 
- Babban Labari - Labarai

Ruwa Ya Yi Gyara A Bunkure 

Rahotanni daga Karamar Hukumar Bunkure a Jihar Kano na cewa mamakon ruwan sama mai karfin gaske da iska sun janyo rushewar gidaje a garin Dogon Jeji.

Rahotanni daga Karamar Hukumar Bunkure a Jihar Kano na cewa mamakon ruwan sama mai karfin gaske da iska sun janyo rushewar gidaje a garin Dogon Jeji.

An bayyana cewa ruwan ya yaye rufin dakuna da yawa in da ya bar masu su cikin halin rashin tabbas.

Malam Isah Muhammad, ya shaida wa Arewa Updates cewa lamarin ya faru ne da yammacin Laraba, inda cikin kankanin lokaci iska da ruwan sama suka yi barna mai tarin yawa.

Malam Isa ya ce, “Gidaje da dama sun rushe, kuma rufin dakuna da yawa sun yaye. Gaskiya jama’a sun shiga cikin wani hali,” .

Abdul Goma wani dan jarida da ke zaune a garin ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa an tafka asara mai yawa.

Wannan dai ba shine karo na farko da ruwa ke yin gyara a yankunan jihar Kano ba a bana.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai