Home » Ruwa Ya Yi Gyara A Bunkure 

Ruwa Ya Yi Gyara A Bunkure 

Rahotanni daga Karamar Hukumar Bunkure a Jihar Kano na cewa mamakon ruwan sama mai karfin gaske da iska sun janyo rushewar gidaje a garin Dogon Jeji.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Rahotanni daga Karamar Hukumar Bunkure a Jihar Kano na cewa mamakon ruwan sama mai karfin gaske da iska sun janyo rushewar gidaje a garin Dogon Jeji.

An bayyana cewa ruwan ya yaye rufin dakuna da yawa in da ya bar masu su cikin halin rashin tabbas.

Malam Isah Muhammad, ya shaida wa Arewa Updates cewa lamarin ya faru ne da yammacin Laraba, inda cikin kankanin lokaci iska da ruwan sama suka yi barna mai tarin yawa.

Malam Isa ya ce, “Gidaje da dama sun rushe, kuma rufin dakuna da yawa sun yaye. Gaskiya jama’a sun shiga cikin wani hali,” .

Abdul Goma wani dan jarida da ke zaune a garin ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa an tafka asara mai yawa.

Wannan dai ba shine karo na farko da ruwa ke yin gyara a yankunan jihar Kano ba a bana.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?