Home » Sanata Barau Ya Jajantawa Al’ummar Jigawa

Sanata Barau Ya Jajantawa Al’ummar Jigawa

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment

Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, SP Barau Jibril Maliya ya jajantawa al’ummar Jigawa  bisa haɗarin tankar mai da ta yi sanadiyyar rasuwar mutane sama da 95 a Majiya dake ƙaramar hukumar Taura a Jihar Jigawa.

Kakakin rundunar yan sandan Jihar, DSP Shaidue Adam ya tabbatar da faruwar lamarin, inda mutane sama da 95 suka rasu, wasu kimanin 50 suka jikkata.

Sanata Barau cikin wata sanarwar da ya fitar ta bakin hadiminsa a ɓangaren yaɗa labarai, Isma’il Mudashir. 

Barau ya bayyana alhininsa da kuma kaɗuwarsa bisa abin da ya faru wa ga mutanen jihar Jigawa. 

“Cikin yanayi na tausayi da alhini, muna miƙa saƙon jaje ga gwamnatin jihar Jigawa da kuma al’ummar jihar, musamman al’ummar garin Majiya da wannan ifti’ai ya faru.

Muna addu’a ga mutanen da suka rasu da kuma addu’ar samun sauƙi ga mutanen da suka jikkata.” 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?