Rahotanni dake fitowa daga jihar Sakoto na cewa masu riƙe da sarautun gargajiya aƙalla 19 ne suka yi murabus domin nuna goyon bayan su ga Sanata Ibrahim Lamido
Waɗanda suka ajiye muƙaman nasu sun haɗa da Dagacin Sabon Birnin Gabas da Tsilba da Faru da Zumbuli da Dawakin da Kanwuri da Hande da Sabon Fegi da Tudun Dankusu da Alhazzai da dai sauransu.
Wannan na zuwa ne makonni kaɗan bayan da Dagacin garin Sabon Birni, Alhaji Abdullahi Muhammad Bawa yayi Murabus.
- Yadda kyautar Ballon d’Or ta bar baya da kura a birnin Paris
- Mabarata Sun Hada Wike Da Allah Kan Hanasu Bara
Takardar wadda ya sa wa hannu, tace, “an naɗa ni Dagacin Sabon Birni a ranar 15 ga watan Yulin 2014, kuma na ajiye muƙami na don na mara wa Sanata Ibrahim Lamiɗo baya.”
Alhaji Lauwali Shu’aibu Dagacin Taka-Tsaba ya ce, mun ajiye muƙaman mu amma ba wanda ya gayyace mu don yaji matsalar mu.