Home » Sarakunan Gargajiya 19 Sun Yi Murabus A Sokoto

Sarakunan Gargajiya 19 Sun Yi Murabus A Sokoto

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment

Rahotanni dake fitowa daga jihar Sakoto na cewa masu riƙe da sarautun gargajiya aƙalla 19 ne suka yi murabus domin nuna goyon bayan su ga Sanata Ibrahim Lamido

Waɗanda suka ajiye muƙaman nasu sun haɗa da Dagacin Sabon Birnin Gabas da Tsilba da Faru da Zumbuli da Dawakin da Kanwuri da Hande da Sabon Fegi da Tudun Dankusu da Alhazzai da dai sauransu.

Wannan na zuwa ne makonni kaɗan bayan da Dagacin garin Sabon Birni, Alhaji Abdullahi Muhammad Bawa yayi Murabus.

Takardar wadda ya sa wa hannu, tace, “an naɗa ni Dagacin Sabon Birni a ranar 15 ga watan Yulin 2014, kuma na ajiye muƙami na don na mara wa Sanata Ibrahim Lamiɗo baya.”

Alhaji Lauwali Shu’aibu Dagacin Taka-Tsaba ya ce, mun ajiye muƙaman mu amma ba wanda ya gayyace mu don yaji matsalar mu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?