Sarkin Musulmi III ya buƙaci ƙungiyar ƙwadago ta janye shiga yajin aiki

Mai alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli a Harkokin Addinin Musulunci, Alhaji Sa’ad Abubakar na uku, ya yi kira ga ƙungiyoyin ƙwadago da su janye batun yajin aiki da zasu shiga a faɗin ƙasar daga ranar Talata 3 ga watan Oktoba.

Sarkin ya bayyana hakan ne a wajen bude taron shirya bikin cikar ƙasar nan shekaru 63 da samun ‘yancin kai wanda ya gudana a jiya Juma’a a birnin tarayya Abuja.

Ya jaddada buƙatar tattaunawa don nemo mafita kan batutuwan maimakon fara yajin aikin ko don maslahar talakawa.

A ƙarshe ya ce yana mai bayar da shawarar tattaunawa ne saboda yajin aikin ba zai magance matsalolin ƙasar nan ba.

Post masu alaƙa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga

JIBWIS Gwallaga Sun Ziyarci A Sansanin Alhazai Na Jihar Bauchi Domin Bada Agaji

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro