Sashen Lura da Basussukan Najeriya, DMO, ya ja hankalin shugaba Tinubu game da ciwo bashi

Sashin lura da al’amuran bashi a Najeriya DMO, ya gargadi gwamnatin tarayya game da ƙarin karbo aron kudi a irin halin da ake ciki.

 Inda ya ce, an fadawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zama dole ya gujewa cin bashi a yanzu.

Hukumar ba ta goyon bayan cin bashin ganin cewa kashi 73.5  na kudin shigar da za a samu a bana duk zai tafi ne a wajen biyan bashin da aka karbo.

Haka zalika hukumar ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta nemi hanyoyin da za tayi wajen ganin ta kara samun kudin shiga a cikin lalitar ƙasar nan.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM