Senegal: Jagoran ‘Yan Adawa, Ousmane Sonko, ya umarci magoyan bayansa su fito zanga-zanga

Jagoran ‘yan adawa a Senegal, Ousmane Sonko ya buƙaci ‘yan kasa su fito kwansu da kwarkwata sun yi zanga-zangar adawa da manufar shugaba Macky Sall ta neman takara a karo na uku.

A yau Litinin ake sa ran shugaba Sall zai gabatar da jawabi domin sanar da anniyarsa ta takara a zaben 2024 ko akasin haka- matakin da akasari kwararu a fannin shari’a ke cewa zai karya ƙundin tsarin mulkin Senegal.

Mista Sanko ya ce ya shafe tsawon shekaru yana fuskantar barazana a rayuwarsa, saboda kwadayin mulki na mutum guda.

A watan da ya gabata, Dubban mutane suka fantsama kan tituna su na zanga-zanga a biranen Senegal bayan yanke hukunci shekaru biyu kan Mista Sonko akan ɓata matasa.

Magoya-bayan Mista Sonko da wasu masu sharhi na ganin wannan hukuncin ƙoƙari ne kawai na datse shi daga takarar shugaban kasa a zaben baɗi.

Post masu alaƙa

AIG Garba Ahmed ya bukaci daliban Sakandaren ’Yan Sanda Dawakin Kudu su zama jakadu na gari.

Venezuela ta sanar da ficewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya

Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu sha da dillancin miyagun ƙwayoyi a Kano – Anti-Phone Snatching Force.