Shugaba Tinubu ya aike wa majalisar dattawa da sunayen ministoci kashi na biyu

Shugaba Bola Tinubu ya mika jerin sunayen ministocinsa kashi na biyu ga majalisar dattawa.

Shugaban ya mika jerin sunayen ne ta hannun Femi Gbajabiamila, shugaban ma’aikatan fadar sa a ranar Laraba.

Izuwa yanzu dai, majalisar ba kai ga bayyana adadin sunayen ke cikin wannan takarda ba kasancewar har yanzu shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio bai karanta ba.

Post masu alaƙa

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wata Mata Mai Shekaru 30 Da Katunan ATM 88

Abubuwa shida da suka sauya tun bayan zaɓen Najeriya na 2023

Kanawa mazauna Abuja sun gudanar da babban taro