Home » Shugaba Tinubu Ya Bada Umurnin Kammala Titin Abuja Zuwa Kano

Shugaba Tinubu Ya Bada Umurnin Kammala Titin Abuja Zuwa Kano

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin kammala aikin babbar hanyar Abuja zuwa Kano cikin wata 12 masu zuwa kamar Yadda Mai magana da yawun fadar shugaban Sunday Dare, ya sanar da Manema labarai

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga: Safiyanu Haruna Kutama

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin kammala aikin babbar hanyar Abuja zuwa Kano cikin wata 12 masu zuwa kamar Yadda Mai magana da yawun fadar shugaban Sunday Dare, ya sanar.

A cewar sa, Shugaba Tinubu ya amince da kasafin kammala wuraren da ba a gama ba a kan titin Abuja-Kaduna, da na Kaduna-Zaria cikin wata 12,” kamar yadda ya wallafa a shafinsa na dandalin X.

A watan Janairu gwamnatin Bola Tinubu ta sanar da bai wa wani sabon kamfani ƙarashen aikin titin bayan ta ƙwace kwangilarsa daga hannun Julius Berger.

Wasu dai na ganin akwai lauje cikin nadi game da Yadda ake tafiyar da aikin hanyar idan aka kwatanta sauran muhimman hanyoyi da ake aikinsu a wasu yankunan kasar nan.

Wasu kuma na ganin akwai sakacin wasu yan majalisun yankin ta yadda suka gaza yin magana da murya daya akan wadannan muhimman ayyuka da zasu karfafa tattalin arzikin yankin Arewacin kasar Najeriya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?