Shugaba Tinubu ya cire sunan Maryam Shetty daga jerin sunayen ministoci

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya cire sunan Maryam Shetty a matsayin wadda za a naɗa kan muƙamin minista, inda ya maye ta da sunayen mutum biyu.

Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ne ya sanar da haka a wata wasiƙa da shugaban ƙasar ya aika wa majalisar kuma ya karanta yayin wani zama a yau.

Sunayen mutum biyu da Shugaba Bola Tinubu ya aika wa majalisar sun haɗar da Festus Keyamo da kuma Dr. Mariya Mairiga.

Ba a dai bayyana dalilin janye sunan Maryam Shetty a jerin ministocin da Tinubun zai naɗa ba

Post masu alaƙa

Dan KAROTA da direba ya buge ya gudu Nasiru Abdullahi Mai Jihadi ya rasu ya bar mata 2 da ‘ya’ya 12.

An kama budurwa ‘yar shekara 15 kan safarar miyagun kwayoyi a Delta.

Uwargidan shugaban Najeriya Sanata Oluremi Tinubu ta kaddamar da rumbum abinci ga jama’ar kudu maso kudancin Najeriya.