Shugaba Tinubu ya cire sunan Maryam Shetty daga jerin sunayen ministoci

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya cire sunan Maryam Shetty a matsayin wadda za a naɗa kan muƙamin minista, inda ya maye ta da sunayen mutum biyu.

Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ne ya sanar da haka a wata wasiƙa da shugaban ƙasar ya aika wa majalisar kuma ya karanta yayin wani zama a yau.

Sunayen mutum biyu da Shugaba Bola Tinubu ya aika wa majalisar sun haɗar da Festus Keyamo da kuma Dr. Mariya Mairiga.

Ba a dai bayyana dalilin janye sunan Maryam Shetty a jerin ministocin da Tinubun zai naɗa ba

Post masu alaƙa

Gwamnati ta buƙaci jama’a su guji taɓa kumfar da ta ɓulla a hanyar Kaduna-Abuja

Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kwace kadarorin Godwin Emefiele

Dalibai huɗu za su wakilci Najeriya a gasar Spelling Bee ta Duniya a China