Home » Sojoji Sun Gano Maboyar Bello Turji 

Sojoji Sun Gano Maboyar Bello Turji 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya ta bakin Babban Jami’in Ayyukanta Manjo-Janar Emeka Onumajuru, ta bayyana cewa saura kiris su gama da jagoran ’yan ta’addan da ya addabi yankin Arewa maso Yamma Kacalla Bello Turji.

Manjo-Janar Emeka Onumajuru ya bayyana cewa sojojin suna kan bibiyar motsin Bello Turji, kuma sun gano inda yake, amma bai yi ƙarin bayani ba.

“Babu wani kwan-gaba-kwan-baya a wurin sojoji kan maganar Bello Turji, mun gano inda maɓoyarsa take,” in ji Janar Emeka.

Ya ci gaba da cewa a halin yanzu sojoji sun riga sun rutsa Turji a maɓoyarsa, babu inda zai iya motsawa ya je, saboda tsoro

Ya bayyana haka ne a safiyar Litinin yana mai cewa kwanakon Turji sun kusa karewa.

Janar din ya bayyana haka ne a yayin hirar da gidan talabijin na Channels ya yi da shi a ranar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?