Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya ta bakin Babban Jami’in Ayyukanta Manjo-Janar Emeka Onumajuru, ta bayyana cewa saura kiris su gama da jagoran ’yan ta’addan da ya addabi yankin Arewa maso Yamma Kacalla Bello Turji.
Manjo-Janar Emeka Onumajuru ya bayyana cewa sojojin suna kan bibiyar motsin Bello Turji, kuma sun gano inda yake, amma bai yi ƙarin bayani ba.
“Babu wani kwan-gaba-kwan-baya a wurin sojoji kan maganar Bello Turji, mun gano inda maɓoyarsa take,” in ji Janar Emeka.
- Gobara Ta Kone Shaguna 103 Da Kayan Abinci A Kasuwar Gusau
- Anya Gwamnati Najeriya za ta iya kula da shirin yaƙi da cutar HIV
Ya ci gaba da cewa a halin yanzu sojoji sun riga sun rutsa Turji a maɓoyarsa, babu inda zai iya motsawa ya je, saboda tsoro
Ya bayyana haka ne a safiyar Litinin yana mai cewa kwanakon Turji sun kusa karewa.
Janar din ya bayyana haka ne a yayin hirar da gidan talabijin na Channels ya yi da shi a ranar.