­­­Sojojin Sudan Sun Yanye Daga Yarjejeniyar Tsagaita Wuta da RSF

Jami’an gwamnatin Sudan sun ce sojojin kasar sun dakatar da tattaunawar dakatar da bude wuta da dakarun kar-ta-kwana na RSF, inda suke zargin ƴan kungiyar da saba yarjejeniyar akai-akai.

Haka kuma wani jami’in diflomasiyya na Sudan sun bayyana wa Reuters, cewa batun janyewar sojojin na Sudan daga tattaunawar yarjejeniyar wadda ake kokarin tabbatarwa domin bayar da damar kai kayan agaji ga wadanda suke matukar bukata

A ranar Litinin masu shiga tsakani daga Saudiyya da Amurka suka ce sojojin da RSF sun amince su tsawaita yarjejeniyar da kwana biyar.

Sai dai kuma an ci gaba da fada a sassa daban-daban na kasar ciki har da babban birnin kasar Khartoum, inda RSf ta ce an kai wa inda dakarunta suke hari.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr