Bola Tinubu

Tinubu ya umarci hafsoshin tsaro su koma Maiduguri

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa hafsoshin tsaro umarnin komawa Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, domin su jagoranci ayyukan tsaro kai tsaye a yankin. Wannan mataki ya biyo bayan hare-haren bama-bamai da suka yi sanadin mutuwar mutane sama da 20 tare da jikkata fiye da 100. Rahotanni daga Maiduguri sun bayyana cewa wasu da […]

Read more

Wane ne sabon sufetan ƴansandan Najeriya Tunji Disu?

Shugaban Najeriya ya sanar da naɗin Olatunji Rilwan Disu a matsayin sufeta-janar na ƴansandan kasar, bayan ajiye aikin tsohon mai riƙe da muƙamin Kayode Egbetokun. A cikin wata sanarwa da fadar shugaban Najeriya ta fitar, Tinubu ya ce ya amince da ajiye aikin Sufeta-Janar Kayode Egbetokun “bayan ya miƙa takardar ajiye aiki bisa dalilai na […]

Read more

Tinubu ya isa Abu Dhabi don halartar taron makamashi

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya isa birnin Abu Dhabi na ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa domin halartar wani taron makon makamashi. Cikin wata sanarwar da fadar shugaban ƙasar ta fitar ta ce Shugaba Tinubu ya samu tarba daga ministan harkokin wajen ƙasar UAE, Sheikh Shakhboot Nahyan Al Nahyan, da jakadan UAE a Najeriya a ƙasar, Salem […]

Read more

Gwamnatin Najeriya ta sha alwashin ƙarfafa dakarun ƙasar

Gwamnatin Najeriya ta alƙawarta sake ƙarfafa dakarun tsaron ƙasar domin magance matsalar tsaro da ke addabar wasu sassan ƙasar. Mataimakin Shugaban Ƙasar, Kashim Shettima ne ya bayyana haka a lokacin taron addu’o’i na musamman ga dakarun tsaron ƙasar da aka gudanar a Babban Masallacin Juma’a na ƙasa da ke Abuja, babban birnin ƙasar. Shettima ya […]

Read more