Bola Tinubu

Tinubu Ya Miƙa Sunan Dambazau A Matsayin Ambasada

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tura ƙarin sunan mutum 4 ɗoriya a kan waɗanda aka fitar a baya zuwa ga majalisar dattawa domin a tantance su a matsayin jakadun ƙasar da za a tura ƙasashen waje. Mutum huɗu da Tinubu ya tura su ne: Ibok-Ete Ekwe Ibas, tsohon shugaban riƙon-ƙwarya na jihar Rivers da tsohon […]

Read more

Tinubu ya rantsar da Chris Musa ministan tsaron Najeriya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya rantsar da Janar Christopher Musa a matsayin ministan tsaron ƙasar bayan amincewar majalisar dattawa. An yi bikin rantsar da tsohon babban hafsan tsaron ne a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja a yau Alhamis, kwana ɗaya bayan ‘yanmajalisar dattawan sun shafe kusan awa biyar suna yi masa tambayoyi yayin tantance […]

Read more

Gwamnan Abia ya ziyarci Tinubu a Villa

Gwamnan jihar Abia, Alex Otti ya ziyarci Shugaba Tinubu a fadar gwamnatin ƙasar da ke Abuja. Duk da cewa babu cikakken bayani game da ziyarar, wasu a ƙasar na ganin ba ta rasa nasaba da batun shugaban ƙungiyar ƴan awaren Biafra, Nnamdi Kanu da aka yanke wa hukuncin ɗaurin rai-da rai cikin watan da ya […]

Read more

Tinubu ya ganawa da manyan hafsoshin tsaron ƙasar

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi ganawar sirri da manyan hafsoshin tsaron ƙasar a fadarsa da ke Villa. Manyan hafsoshin sun isa fadar shugaban ƙasar da maraicen yau Talata, inda suka yi ganawa har ta tsawon sa’o’i uku, kamar yadda jaridun ƙasar suka ruwaito. Ba a dai bayyana dalilin ganawar ba, amma wasu na ganin […]

Read more

Tinubu ya nemi tura ƙarin jakadu 32 zuwa ƙasashen waje

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya miƙa wa majalisar dattawa sunayen mutum 32 da yake son turawa a matsayin jakadun ƙasar zuwa ƙasashen waje. Wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar a yau Asabar ta ce shugaban ya nemi majalisar ta gagaggauta tantancewa da amincewa da mutanen. Sunayen sun ƙunshi Femi Fani-Kayode, tsohon ministan sufurin […]

Read more

Tinubu Ya Aiyana Dokar Ta Baci Kan Tsaro A Nijeriya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a faɗin ƙasar, yana mai bayar da umarnin ɗaukar ƙarin jami’an ‘yansanda da na soja. Shugaban wanda ya bayar da umarnin yayin wani jawabi a fadarsa, ya bai wa rundunar ‘yansandan ƙasar umarnin ɗaukar ƙarin jami’ai 20,000. Ya ce adadin sababbin jami’an da za […]

Read more

Tinubu Ya Gana Da Shugaban Ƙasar Saliyo A Abuja

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya gana da takwaransa na ƙasar Saliyo, Shugaba Julius Maada Bio, a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, da yammacin Juma’a. Shugaba Bio ya isa fadar Villa da misalin ƙarfe 9:08 na dare, inda aka yi masa tarɓar ban girma, kafin ya wuce ofishin Shugaba Tinubu domin gudanar da ganawar […]

Read more