Majalisa Za Ta Binciki Zargin Rashin Ingancin Matatar Man Dangote
Shugaban Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abbas ya ce za a gudanar da bincike kan zargin da ake yi cewa man fetur ɗin da ake samu daga matatar Dangote bai kai kyau da ingancin wanda ake shigowa da shi daga ƙasashen ƙetare ba.


