Matan da ke gabatar da shirin ‘Mata A Yau’ sun ziyarci hukumar Hisbah
Matan da ke gabatar da shirin ‘Mata A Yau’ a wani gidan talabijin a nan Kano, sun ziyarci shugaban hukumar Hisbah Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa a daidai lokacin da ake tafka muhawara kan wasu kalaman da suka yi, a cikin shirin dangane da batun gaisuwa tsakanin mata da miji.