Nigeria

Tinubu Ya Buƙaci NAHCON Ta Rage Kuɗin Hajjin Bana

Sakamakon kokawar da al’ummar Nijeriya ke yi kan tsadar kudin kujerar  aikin hajjin bana shugaban kasar Bola Tinubu ya buƙaci hukumar jin daɗin alhazai ta Najeriya NAHCON da ta rage kuɗin Hajjin bana, inda ya buƙaci hukumar ta fito da sabon kuɗin nan da kwana biyu. Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ne ya bayyana wannan […]

Read more

Babu Inda Na Ce Zan Janye Wa Wani Takarata – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin da ke cewa zai janye wa wani takararsa a zaɓen shugaban ƙasa mai zuwa. Wannan na zuwa ne bayan wata hira da Atiku yayi da BBC Hausa a ranar Laraba, 1 ga watan Oktoban 2025, ranar da Najeriya ke bikin cika shekara 65 da samun ƴancin […]

Read more

Ɗalibar Jami’ar IBB Ta Faɗi Ta Rasu

Wata ɗalibar aji biyu a sashen nazarin ƙwayoyin halittu da sunadarai na Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBBU), Lapai da ke Jihar Neja ta riga mu gidan gaskiya. Aminiya ta ruwaito cewa, Fatima Adamu Muhammad, ta rasu ne bayan ta yanke jiki ta faɗi a wani matsuguninta da ke wajen makarantar. Rahotanni sun ce ta fara […]

Read more

An Kama Buhunan Tabar Wiwi Da Dillalansu 11 A Abuja

Rundunar ‘yansandan Najeriya reshen birnin Abuja ta ce ta kama mutum 11 da zargin safarar miyagun ƙwayoyi a wasu samame da ta kai a wasu lokunan birnin. Wata sanarwa a shafukan sada zumunta ta ce samamen sun kai ga gano buhun tabar wiwi 68. “Kamen wani ɓangare ne na yunƙurin daƙile ayyukan safara na gungun […]

Read more

An Sanar Da Kuɗin Aikin Hajji Na 2026 A Najeriya

Hukumar aikin Hajji ta Najeriya (NAHCON) ta sanar da farashin kujerar aikin Hajjin bana. Sabon farashin aikin Hajjin na shekarar 2026 miladiyya ya nuna cewa an samu ɗan ragi idan aka kwatanta da na 2025. Shugaban hukumar farfesa Abdullahi Saleh Usman, wanda ya sanar da hakan a wata hira da BBC daga birnin Makka na […]

Read more

Ba Mu Nemi Shiga Wata Jam’iyya Ba – Kwankwaso

Tsohon gwamnan Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta rahotannin da ke yawo a shafukan sada zumunta da ke cewa ya tura takardar neman shiga wata jam’iyyar siyasa a ƙasar. Ya bayyana cewa labarin ba gaskiya ba ne, yana mai jaddada cewa ba su nemi shiga wata jam’iyya ba. Wannan na zuwa […]

Read more