Najeriya Ta Jaddada Kudirin Ta Na Inganta Samar da Abinci a Duniya A Taron UNGA80

 

Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Noma da Samar da Abinci ta Ƙasa, Dakta Marcus Ogunbiyi, ya jagoranci tawagar Najeriya zuwa Taron Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA) karo na 80 a Sashen Kwamiti na Biyu da ke kula da Harkokin Tattalin Arziki da Kuɗi a birnin New York.

Tawagar ta Najeriya ta halarci zama na fasaha kan noma, samar da abinci da kuma abinci mai gina jiki, inda suka jaddada aniyar Najeriya wajen taka muhimmiyar rawa a ƙoƙarin duniya na magance yunwa da rashin abinci mai gina jiki.

Dakta Ogunbiyi ya bayyana manufofi da shirye-shiryen da ake aiwatarwa a Najeriya domin ƙarfafa noma, samar da kayan aiki ga manoma, da kuma tabbatar da juriyar tsarin abinci kan matsalolin da sauyin yanayi ke haifarwa.

Ya ce, Najeriya na aiki ba kawai don tabbatar da wadatar abinci ga ‘yan ƙasa ba, har ma da taka muhimmiyar rawa wajen tsara hanyoyin dorewa don magance ƙalubalen samun abinci a duniya.

Post masu alaƙa

Yan sanda sun kama mutane 79 tare da kwato kwayoyi da makamai a bikin Takutaha a Kano.

Yan sanda sun kama wanda ake zargi da damfarar masu neman aikin gwamnati Naira miliyan 40.

Sabuwar majalisar gudanarwa ta POLAC za ta mayar da hankali kan inganta da ilimi da horo.