Sojojin Najeriya sun ce sun tseratar da matafiya 23 daga masu garkuwa a Kogi
Rundunar sojin ƙasan Najeriya ta ce jami’anta sun samu nasarar tseratar mutum 23, waɗanda ta ce matafiya ne da ƴanbindiga suka tare a babbar hanyar Ayegunle zuwa Bunu da ke jihar Kogi, kamar yadda jaridar Guardian mai zaman kanta ta ruwaito a ranar Asabar 6 ga Yuni. Rahotanni sun bayyana cewa ƴanbindiga sun tare hanyar […]










