Tinubu ya isa Kenya don halartar taron ƙoli na Afirka da Faransa

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya isa Nairobi, babban birnin Kenya gabanin taron ƙoli na Afirka da Faransa da za a shafe yini biyu ana yi.

Shugaba Tinubu ya samu tarba daga jami’i a gwamnatin Kenya, Musalia Mudavadi wanda kuma shi ne sakataren da ke kula da harkokin da suka shafi ƙasashen ƙetare.

Akwai kuma Ministar harkokin waje ta Najeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu da Jakadan Kenya a Najeriya, Amb. Isaac Parashina.

Taron zai ƙara ƙarfafa ƙudirin Najeriya na zurfafa alaƙa da kuma haɗin kai da sauran ƙasashen Afirka da kuma Faransa.

Post masu alaƙa

An kama wasu mutum 7 da ake zargin ƙusoshin Boko-Haram ne a filin jirgin Katsina

KACRAN ya ti watsi da ƙirƙiro ƴansandan jihohi a Najeriya

INEC na shirin cire NDC daga rajistar jam’iyyun siyasa bayan hukuncin kotu