Tinubu ya isa Kenya don halartar taron ƙoli na Afirka da Faransa

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya isa Nairobi, babban birnin Kenya gabanin taron ƙoli na Afirka da Faransa da za a shafe yini biyu ana yi.

Shugaba Tinubu ya samu tarba daga jami’i a gwamnatin Kenya, Musalia Mudavadi wanda kuma shi ne sakataren da ke kula da harkokin da suka shafi ƙasashen ƙetare.

Akwai kuma Ministar harkokin waje ta Najeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu da Jakadan Kenya a Najeriya, Amb. Isaac Parashina.

Taron zai ƙara ƙarfafa ƙudirin Najeriya na zurfafa alaƙa da kuma haɗin kai da sauran ƙasashen Afirka da kuma Faransa.

Post masu alaƙa

Gwamnati ta tilasta yi wa ɗaliban sakandare gwajin ƙwaya a Najeriya

SDP ta zaɓi Farfesa Sadiq Gombe a matsayin Shugaban Jam’iyya na Ƙasa

Muna kashe N150m duk wata kan samar da ruwa —Gwamnan Gombe