Home » Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yammacin Najeriya

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yammacin Najeriya

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya naɗa shugabannin sabuwar Hukumar Raya yankin Arewa-maso-yammacin Najeriya.

Bola Ahmad Tinubu ya miƙa wa Majalisar Dattawa sunayen shugabannin sabuwar Hukumar Raya Yankin Arewa-maso-yamma domin samun sahalewarsu.
Wannan na zuwa ne bayan sanya hannu kan dokar da ta kafa hukumar da shugaban ƙasa ya yi a ranar 24 ga watan Yulin 2024.

Shugabannin da shugaban ƙasa ya miƙa sunayensu ga Majalisar su ne:

Shugaba: Ambassador Haruna Ginsau (Jigawa)

Manajin darakta: Professor Abdullahi Shehu Ma’aji (Kano)

Sauran lambobin hukumar:

– Dr. Yahaya Umar Namahe (Sokoto)

– Hon. Aminu Suleiman (Kebbi)

– Sen. Tijani Yahaya Kaura (Zamfara)

– Hon. Abdulkadir S. Usman (Kaduna)

– Hon. Engr. Muhammad Ali Wudil (Kano)

– Shamsu Sule (Katsina)

– Nasidi Ali (Jigawa)

Ana sa ran wannan sabuwar hukuma za ta mayar da hankali wajen samar da cigaba ga ɓangaren tattalin arziƙi da bunƙasa rayuwar al’ummar wannan yanki.

Wannan sanarwa ta fito ne daga bakin mataimaki na musamman ga shugaban ƙasa kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga wacce ya fitar a yau 28 watan Satumba, 2024.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?