Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da Gwamna da mataimakinsa da daukacin ’yan Majalisar Dokokin Jihar Ribas, tare da ayyana dokar ta-baci a Jihar.
Tinubu ya kuma ayyana Navy Vice Marshal Ibok-Ete Ekwe Iba a matsayin Gwamnan Rikon Jihar Ribas, a yayin jawabinsa ga ’yan Najeriya game da harin da aka kai wa bututun man fetur a Jihar.
“Ina amfani da tanadin kundin tsarin mulkin Nijeriya wajen ayyana dokar ta-baci da kuma dakatar da gwamnan da mataimakinsa da zabbabbun ’yan majalisar na tsawon wata shida, daga yau 18 ga watan Maris, 2025” in ji shugaban kasan.
- Masarautar Hadejia Ta Jajantawa Iyalan Wadanda Suka Rasa Yan Uwansu
- Wike Ya Kwace Filin Sakatariyar PDP A Abuja
Ya sanar da hakan ne jim kadan bayan shan ruwa a ranar Talata, ’yan sa’o’i bayan wani zaman gaggawa da ya yi da manyan hafsoshin tsaro a sakamakon harin da ’yan ta’adda suka kai kan bututun mai na Trans-Niger Pipeline (TNP) da ke yankin Bodo da ke Karamar Hukumar Gokana ta Jihar Ribas.
Mahara sun kai harin ne bayan barazanar yin hakan da suka bayar a makon jiya a sakamakon kara tsanani da rikicin shugaban jihar ya yi tsakanin ’yan majalisar da kuma gwamna Simi Fubara.
Ibok-Ete Ibas shi ne tsohon Babban Hafsan Sojin Ruwa na Nijeriya daga shekarar 2015 zuwa 2021 a zamanin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

