Tsohon Shugaban Kasa, Goodluck Jonathan, Ya Karyata Zargin da Femi Kuti Ya Yi Masa

Tsohon Shugaban Kasa, Goodluck Jonathan, Ya Karyata Zargin da Femi Kuti Ya Yi Masa

Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya musanta iƙirarin da Femi Kuti ya yi a kansa, wanda ya ce Hukumar EFCC mai yaƙi da yi wa arziƙin ƙasa ta’annati ta gayyace shi kan zargin sha’anin kuɗi bayan wa’adinsa ya ƙare a matsayin mataimakin gwamnan Jihar Bayelsa.

A baya-bayan nan mawaƙin ya ce tsohon shugaban Najeriya ya taɓa zuwa EFCC a matsayin wanda aka yi wa tambayoyi ko gudanar da bincike a kan shi, sai dai wata sanarwa da tsohon shugaban ya fitar ta musanta hakan.

A jiya Juma’a ne Wealth Dickson Ominabo jami’in yaɗa labarai ne a ofishin tsohon shugaban ƙasar ya fitar da sanarwar da ta ƙaryata wannan iƙirari.

Inda ya ce ya yi amfani da wasu bayanai da wasu suka riƙa yaɗa wa a baya kan tsohon shugaban kasar domin su ɓata masa sunan, har suka riƙa cewa sai da ya je EFCC domin amsa tambayoyi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *