Ukraine ta gano gawarwakin ƴan Najeriya da aka kashe cikin sojojin Rasha

Hukumar leƙen asirin Ukraine, UDI ta bayyana cewa ta gano wasu ƴan Najeriya biyu da aka kashe a matsayin sojojin hayar Rasha a yayin farmakin da suka kai yankin Luhansk.

Hukumar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar jiya tare da hotunan mutanen, inda ta nuna su kafin mutuwarsu da kuma wani hoto da ya shafi iyalan ɗaya daga cikinsu.

Wannan na zuwa ne makonni biyu bayan samun labarin rasuwar wani matashi a Kano wanda ake zargin ya shiga aikin sojin haya na ƙasar Rasha.

Bayanan da jami’an leƙen asirin sojin Ukraine a yankin Luhansk suka fitar sun bayyana sunayen mutanen da Hamzat Kazeen Kolawole da kuma Mbah Stephen Udoka.

Sanarwar ta ƙara da cewa mutanen biyu sun yi aiki a bataliyar sojin Rasha ta 423 mai kula da tankokin yaƙi.

Rahotanni na cewa ba su kaɗai ba ne suka shiga aikin soja a Rasha, domin akwai ƴan Najeriya da dama, ciki har da wasu daga Kano.

Post masu alaƙa

An kashe kwamandojin ’yan bindiga biyu a Katsina

NAPTIP ta ceto sama da yara 180 da ake safararsu ta hanyar ƙungiyoyin fara hula na bogi

Nafi’u ya gargaɗi Atiku ya daina sukar Tinubu da sunan ADC