INEC ta saka ranar zaɓen 2027

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya Inec ta fitar da jadawalin manyan zaɓuɓɓukan kasar na shekarar 2027, inda ta bayyana muhimman ranakun zaɓe da na zaɓen fidda gwani na jam’iyyun siyasa da yakin neman zaɓe, da rajistar masu zaɓe.

Hukumar ta ce za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar tarayya ranar Asabar, 20 ga Fabrairun 2027, yayin da zaɓen gwamna da na majalisun jihohi za su biyo baya bayan makonni biyu, wato ranar 6 ga Maris, 2027.

Game da yakin neman zaɓe kuma, jam’iyyun siyasa da ‘yan takara za su fara yakin neman zaɓe na shugaban ƙasa da majalisar tarayya daga ranar 18 ga Nuwambar 2026 zuwa 19 ga Fabrairun 2027.

Yakin neman yakin zaɓen gwamnoni da na majalisun jihohi zai fara daga ranar 15 ga Disambar 2026 kuma zuwa 5 ga Maris, 2027, awanni 24 kafin ranar zaɓe.

Haka kuma, jam’iyyun siyasa za su gudanar da zaɓen fidda gwani tsakanin 1 ga Yuli da 30 ga Satumbar 2026, sannan su miƙa sunayen ‘yan takararsu a ranakun tsakanin 1 da 31 ga Oktobar 2026.

Hukumar ta ƙara da cewa za ta fitar da jerin sunayen ‘yan takara na ƙarshe ranar 15 ga Nuwambar 2026,

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda