Wani dogon gini ya rufta a Abuja tare da danne mutane da dama

Akalla mutum biyu sun mutu sakamakon ruftawar wani bene mai hawa biyu a unguwar Garki da ke tsakiyar birnin tarayyar Najeriya Abuja.

Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa na birnin Abuja, Abbas Idris, ya tabbatar wa da manema labarai kan faruwar al’amarin, inda ya ce jami’an su na ci gaba da aikin ceto a wurin da lamarin ya faru.

Abbas Idris ya ce kawo yanzu an zaƙulo mutane 37 daga cikin ginin, inda mutum biyu suka mutu, sannan an garzaya da wasu 35 zuwa asibiti.

Tuni jami’an ceto daga hukumomin bayar da agajin gaggawa na FEMA, da jami’an kashe gobara da haɗin gwiwar jami’an kiyaye aukuwar haɗura ta ƙasar, FRSC suka isa wurin domin tabbatar da aikin ceto waɗanda suka maƙale a ƙarƙashin ginin.

Kawo yanzu dai hukumomin ba su bayyana abin da ya haddasa ruftawar ginin ba.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr