Wasu Matasa Sun Kashe Ɗan Sanda a Lokacin da Yake Raba Faɗa

Wasu matasa sun kashe wani dan sanda da yake kokarin raba fada tsakanin wasu kungiyoyi da ba sa jituwa da juna a Karamar Hukumar Lavun da ke Jihar Neja.

Dan sandan wanda aka bayyana sunansa da Nasiru, an kashe shi ne a kauyen Manima na unguwar Gaba da ke yankin.

Rahotanni na nuni da cewa, bayan barkewar rikicin, an gayyato jami’an tsaro, inda bayan zuwansu, sai mambobin kungiyoyin suka sare shi da makamai a ka.

Wani mazaunin yankin ya shaida wa wakilinmu cewa kafin faruwar lamarin, dan sandan ya halarci wani taron zama lafiya a kauyen Doko na Karamar Hukumar ta Lavun, inda aka tattauna batun yawan faruwar rikice-rikice kan filaye a yankin.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar NEJA, DSP Wasiu Abiodun, ya ce tuni suka kama mutum biyu da ake zargi da hannu a lamarin.

Post masu alaƙa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga

JIBWIS Gwallaga Sun Ziyarci A Sansanin Alhazai Na Jihar Bauchi Domin Bada Agaji

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro