Home » Wata gobara ta ƙone sansanin ‘yan gudun hijira a Barno

Wata gobara ta ƙone sansanin ‘yan gudun hijira a Barno

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumar Bunƙasa Yankin Arewa-maso-gabas, wato North East Development Commission, ta kai kayan agajin gaggawa ga mutanen da suka gamu da ibtila’in gobara a sansanin ‘yan gudun Hijrah na Rundaben Shuwa da ke kusa da Bauchi.

Wannan al’amari ya faru ne a lokacin da ake sallar juma’a bayan da wata  mummunar gobara ta tashi daga wani gida inda ta wutar ta watsu zuwa wasu gidajen a ƙalla  20 waɗanda yawanci gidajen kara ne, tare da ƙone su kurmus.

Sama da mutane 100 ne suka  tagayyara sakamakon wannan gobara, inda wasu suka koma bukkokin ‘yan uwa da je sansanin da barandar masallaci domin zama da iyalansu kafin isowar kayan agaji.

Ga  Mu’azu Hardawa Bauchi da cigaban wannan labari:

Bayan kashe wutar, an yi jana’izar wani magidanci wanda ya rasa ransa, a ƙarƙashin jagorancin tawagar shugaban ‘yan gudun Hijra Buba Musa Shehu, tare da binne shi a makabartar Dungulbe.

 

 

 

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?