Home » ‘Yan Bindiga Sun Sake Sace Mutane 8 a Kaduna

‘Yan Bindiga Sun Sake Sace Mutane 8 a Kaduna

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Kaduna

Wasu ‘yan bindiga a sanyin safiyar nan sun kai wani sabon hari garin Dogon-noma da ke ƙaramar hukumar Kajuru da ke jihar Kaduna.

Wannan hari na zuwa ne kwanaki uku bayan kashe wani mutum ɗaya da yin garkuwa da mutane 8 a garin Banono Angwaku  da ke ƙaramar hukumar ta Kajuru.

Tsohon shugaban ƙaramar hukumar, Cafra Caino, ne ya tabbatar da kai wannan hari ga manema labarai.

A cewarsa, masu kai harin sun kai samamen ne da asuba tare da yin harbe-harben kan mai uwa dawabi.

A yayin da aka tuntuɓi jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mansir Hassan, kan wannan al’amari, ya sanar da majiyarmu kan cewa su turo masa da saƙon kar ta kwana saboda yana tuƙi, amma har zuwa sanda muke haɗa muku wannan rahoto bai kai ga yi mana ƙarin haske ba.

Ƙananan hukumomin Kajuru da Chikun na jihar Kaduna dai su ne kan gaba a ‘yan kwanakin nan wajen fuskantar hare-haren ‘yan bindiga da kuma garkuwa da mutane.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?