Home » Wata kungiya a Najeriya ta bukaci shugaba Tinubu ya gujewa bai wa tsofaffin gwamnoni ministoci

Wata kungiya a Najeriya ta bukaci shugaba Tinubu ya gujewa bai wa tsofaffin gwamnoni ministoci

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Wata kungiya a Najeriya ta bukaci shugaba Tinubu ya gujewa bai wa tsofaffin gwamnoni ministoci

Kungiyar Matasan Kudu Maso Yammacin ƙasar nan ta bukaci shugaba Bola Ahmad Tinubu da kada ya naɗa wani tsohon gwamna mukamin minista a gwamnatinsa.

Shugaban kungiyar, Kwamared Funsho Ajimuda ne ya bayyana hakan ga manema labarai a cikin wata sanarwa da ya fitar ajiya Asabar. Inda Ya zargi tsoffin gwamnonin da lafta wa jihohinsu basukan na bagaira ba dalili.

Ya ce, “Kamar yadda ake ta yamaɗidin cewar, wasu gwamnoni da dama na ta neman mukaman minista da wasu mukamai. Babu komai a cikin hakan illa tsagoran son kai da son zuciya bayan da suka shafe shekaru takwas a matsayin gwamnoni amma sun bige da neman kujerar minista.

Wannan kungiya na fatan za a yi watsi da wannan bukatar ta tsoffin gwamnonin a matsayin ministoci.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?