Wata kungiya a Najeriya ta bukaci shugaba Tinubu ya gujewa bai wa tsofaffin gwamnoni ministoci

Kungiyar Matasan Kudu Maso Yammacin ƙasar nan ta bukaci shugaba Bola Ahmad Tinubu da kada ya naɗa wani tsohon gwamna mukamin minista a gwamnatinsa.

Shugaban kungiyar, Kwamared Funsho Ajimuda ne ya bayyana hakan ga manema labarai a cikin wata sanarwa da ya fitar ajiya Asabar. Inda Ya zargi tsoffin gwamnonin da lafta wa jihohinsu basukan na bagaira ba dalili.

Ya ce, “Kamar yadda ake ta yamaɗidin cewar, wasu gwamnoni da dama na ta neman mukaman minista da wasu mukamai. Babu komai a cikin hakan illa tsagoran son kai da son zuciya bayan da suka shafe shekaru takwas a matsayin gwamnoni amma sun bige da neman kujerar minista.

Wannan kungiya na fatan za a yi watsi da wannan bukatar ta tsoffin gwamnonin a matsayin ministoci.

Post masu alaƙa

An kashe kwamandojin ’yan bindiga biyu a Katsina

Yan Sandan a Kano sun kama mutane 244, ciki har da 117 da ake zargi da fadan daba.

Ƴansanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a bikin Takutaha, tare da gargaɗin masu yunkurin tada zaune tsaye.