Siyasa

Barau Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Arewa A APC

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau I. Jibrin, ya zama ɗan takarar Sanatan Kano ta Arewa na jam’iyyar APC mai mulki. An gudanar da taron tabbatar da takararsa a hedikwatar APC da ke Bichi, inda dubban magoya baya daga ƙananan hukumomi 13 na yankin suka halarta. Bayan kammala taron, Barau ya gode wa magoya bayan jam’iyyar […]

Read more

Sanata ya bar APC a jajibirin zaɓen fidda gwani a Kebbi 

Sanatan Kebbi ta Kudu a Majalisar Dattawa, Garba Musa Maidoki, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar APC. A cikin wata wasiƙa da ya aike wa Shugaban APC na mazaɓar Rafin Zuru mai ɗauke da kwanan watan 14 ga Mayu, 2026, Sanatan ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon rikice-rikicen cikin gida da suka dabaibaye jam’iyyar. […]

Read more

Yusuf Buhari ya lashe zaɓen takarar majalisar tarayya a APC

Yusuf Buhari, ɗan tsohon shugaban Najeriya marigayi Muhammadu Buhari, ya samu nasara a zaben fitar da gwani na jam’iyyar APC na mazabar Sandamu/Daura/Mai’adua. Da yake bayyana sakamakon zaɓen, shugaban kwamitin zaɓe na mazabar, Lawan Garba, ya ce Yusuf Buhari ya samu ƙuri’u 17,342, inda ya doke abokin takararsa, Auwalu Musa Daura, wanda ya samu ƙuri’u […]

Read more

Tsohon Shugaban ’Yan Sanda ya janye daga takarar Gwamnan Yobe

Tsohon Shugaban ’Yan Sandan Najeriya, Usman Baba Alƙali, ya sanar da janyewarsa daga neman takarar Gwamnan Jihar Yobe. Usman Baba Alƙali wanda ke neman takarar Gwamnan Yobe a ƙarƙashin inuwar Jam’iyyar APC, ya sanar da haka ne ta wata takardar sanarwa da ya fitar a ranar Laraba. Ya bayyana cewa ya yanke shawarar janyewa ne […]

Read more

Jam’iyyar NDC na gudanar da babban taronta na ƙasa

Jam’iyyar hamayyar ta NDC a Najeriya na gudanar da babban taronta na ƙasa domin zaɓen sabbin shugabanninta. Matakin na zuwa ne mako guda bayan da manyan jiga-jigan siyasar ƙasar biyu, Peter Obi da Kwankwaso suka sanar da komawa cikinta. Ɗaruruwan magoya bayan jam’iyyar ne suka taru a harabar wurin gudanar da taron a Abuja. Akwai […]

Read more

Kwankwaso da Obi za su fice daga ADC

Ranar Litinin Kwankwaso da Obi za su fice daga ADC – Buba Galadima Sakatare a kwamitin amintattu na jam’iyyar NNPP kuma jigo a tafiyar Kwankwasiyya, Injiniya Buba Galadima, ya bayyana a ranar asabar cewa ranar Litinin Sanata Kwankwaso da Peter Obi za su fice daga jam’iyyar ADC, Buba Galadima ya kara da cewa za kuma […]

Read more

Ana hasashen yiwuwar rikici tsakanin Amurka da Iran Ana ci gaba da nuna damuwa kan yiwuwar sake barkewar rikici tsakanin Amurka da Iran, bayan da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana rashin gamsuwarsa da bukatun da Iran ta gabatar a tattaunawar da ke gudana. Wani babban jami’in soja a Iran ya yi gargadin cewa akwai […]

Read more