WHO na neman ƙarin kuɗi don daƙile Ebola a Congo

Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya na neman ƙarin kuɗi don taimaka wa Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo don ta samu ta yaƙi ɓarkewar cutar Ebola.

Da yake magana a Kinshasa, Tedros Adhanom Ghebreyesus ya ce kashi ɗaya bisa uku na tallafin da ake nema aka samu zuwa yanzu.

Amurka ta yi alƙawarin bayar da ƙarin dala miliyan 80 domin tallafa wa ƙoƙarin da ake a Congo da Uganda inda aka tabbatar da wasu mutum bakwai sun kamu da cutar.

WHO ta ce mutum na farko da ya warke daga cutar tuni aka sallame shi daga asibiti.

Cutar ta kashe fiye da mutum 200 inda ake zargin dubbai sun kamu da cutar.

Post masu alaƙa

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya

Rundunar yan sandan jihar Kano ta kama dan bindiga da sanye da kayan sojoji.

Majalisar Wakilai ta janye kudirinta kan ‘yan sandan jihohi tare da yin nazari kan buƙatar Tinubu